Sababbin alkalumma da ke fitowa daga hukumomin jamhuriyar Kamaru na nuna cewa kawo yanzu adadin 'yan kasar da suka rasa rayukansu a turmutsutsun da aka yi a Muna a kasar Saudi Arabia lokacin aikin hajjin bana, ya kai 76 sannan wasu da dama sun jikkata a inda kuma har yanzu ba aji duriyar wasu ba.

Gwamnatin kasar dai ta ayyana yau Juma'a domin ta zamo ranar nuna alhini dangane da rashin da kasar ta yi. Ku saurari Usman Minjibi da wikilinmu Muhammad Babalala domin jin karin bayani.