Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya ta ce mutane 30 ne aka kashe yayinda da dama suka ji raunuka a hare haren kunar bakin wake da wasu da ake zargin mayakan kungiyar Boko Haram ne suka kai a gaban wani masallaci a unguwar Mulai a birnin Maiduguri. Ku saurari rahoton da wakiliyarmu Raliya Zubairu ta hada mana domin jin karin bayani.