A kasar Guinea 'yan takarar shugaban kasa bakwai na bangaren adawa sun ce, ba zasu amince da sakamakon zaben shugaban kasar ba, kuma sun yi kiran ayi sabon zaben.
Sun dai zargi hukumar zaben kasar da hada baki da jam'iyya mai mulki wajen murde zaben da aka yi ranar Lahadi.
Ku saurari fassarar rahoton Abdourahmane Dia daga birnin Dakar, domin jin karin bayani.