Shugaba Muhammadu Buhari ya bukaci Birtaniya da ta kara kokari wajen tallafawa Najeriya ta fuskar tsaro musamman wajen samar da taimakon kayan yaki da kuma hanyoyin tattara bayanai na tsaro.

Ku saurari hirar wakilinmu Isa Sanusi da Malam Garba Shehu, shi ne babban mataimaki na musamman ga shugaba Buhari ta fuskar yada labarai, domin karin bayani.