Rahotanni daga garin Mungono na Jihar Borno na cewar wani harin kunar bakin wake da wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai ya halaka mutane 32, kuma mutane 29 sun samu rauni. Ku saurari hirar da BBC ta yi da Dan Civilian JTF ko kato da gora na Garin Mungono.