Hukumar agajin gaggawa ta kasa a Nigeria NEMA ta ce mutane 28 ne suka mutu wasu arba'in da hudu suka jikkata bayan fashewar wani bam a wata kasuwar sayar da wayoyin hannu dake garin Sabon Gari kusa da Damboa a jihar Borno. Ku saurari tattaunawar da Ahmed Abba Abdullahi ya yi da Alhaji Muhammadu Kanar, shugaban hukumar ta NEMA a shiyyar Arewa maso gabas.