Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada wani kwamitin da zai ba shi shawara kan yadda zai yaki cin hanci da rashawa. Farfesa Sadik Isa Radda shaihin malami a fannin nazarin miyagun laifukka a jami'ar Bayero da ke Kano na daya daga cikin mambobin wannan kwamiti, ku saurari hirarsa da Ibrahim Mijinyawa.