Daruruwan matafiya da ababen hawansu sun rasa na yi a kan babban titin da ya hada jihar Zamfara da makwabtan jihohin Sakkwato da Kebbi sakamako ruftawar wata gada a kan wannan titin. Gadar, wadda aka fi sani da gadar Danmarke ta auka ne jiya bayan da aka kwashe wasu sa'o'i ana tafka ruwan sama.