Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yace matakin da Amurka ta dauka na rashin sayarwa da Najeriya makamai bisa zargin keta haddin bil Adama da ake yiwa sojojin Najeriya wanda ba'a tabbatar da shi ba ya kawo nakasu wajen yaki da Boko Haram. Ku saurari hirar wakilinmu Abdullahi Tanko Bala da Dr Aliyu Musa malami a Jami'ar Coventry a Birtaniya domin jin karin bayani.