A yau Litinin ne tashar watsa labarai ta BBC a yankin Afrika take fara kawo muku jerin rahotanni na tsawon mako guda da suka shafi cututtukan da nahiyar ke fama da su wadanda mutane basa iya yada su ga wasu ta hanyar mu'amala. Wakiliyarmu Tchima Illa Issoufou ta duba mana matsalar Hawan jini a jihar Tahoua ta jamhuriyar Nijar, ku saurari rahoton da ta hada mana