Shugaba Muhammadu Buhari ya aika takarda zuwa majalisar dattijai domin neman amincewarta ya nada mukaman mataimaka na musamman 15 a gwamnatinsa. Ku saurari tattaunawar da wakilinmu Yusuf Ibrahim Yakasai ya yi da Farfesa Umar Pate na sashen nazarin aikin jarida a jami'ar Bayero da ke Kano.